31 Yuli 2015 - 10:26
Wata ta kai harin kunar bakin wake a Maiduguri

Wata ‘Yar kunar bakin wake ta tayar da bom a kasuwar Gamburo kwastam a garin Maiduguri cikin keke Napep da safiyar yau Juma’a.

Ruhotanni kimanin mutane biyar suka mutu tare da jikkata wasu da dama, kuma adadin wadanda suka mutu na iya karuwa.

‘Yar Kunar bakin waken ta kai harin ne sanye da hijabi cikin karamar mota mai kafa uku da ake kira Keke napep.

Zuwa yanzu Jami’an tsaro sun killace inda aka kai harin a garin Maiduguri.288